Gwamnatin Kano ta kori daraktocin ma’aikatar tattara kudade guda 8

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya amince da korar wasu daraktoci 8 daga hukumar tara haraji ta Kano.

Wata takardar sanarwa mai dauke da kwanan watan 18 ga watan Janairun 2024 ta ce matakin na daga cikin kokarin da ake yi na cimma muradun gwamnatin da ake so a yanzu.

Takardar wadda ke dauke da sa hannun Hamisu Sule Garko, Babban Daraktan Ayyuka na Tallafawa, a madadin Shugaban KIRS, Sani Abdulkadir Dambo, ta umurci Daraktocin da abin ya shafa da su mika ragama ga mataimakansu nan take.

“A ci gaba da kokarin da ake yi na cimma manufofin gwamnati mai ci, an umurce ni da in sanar da ku cewa an sauke Daraktocin da ba aka ambata daga mukamansu, kuma za su mika su ga mataimakansu nan take.

“Daraktocin da abin ya shafa sun hada da Daraktan tantancewa Muhammad Kabir Umar; Daraktan Ma’aikata, Kabiru Magaji; Daraktan Kasuwancin Gwamnati, Ibrahim Sammani; Daraktan Harajin titi da sauransu, Aminu Umar Kawu; da daraktan binciken haraji, bincike da kula da basussuka, Muhammad Auwal Abdullahi.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...