Gwamnatin Kaduna za ta gina gidaje 10,000 a cikin shekaru 4

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce za ta gina gidaje masu sauki 10000 a cikin shekaru huÉ—u masu zuwa.

Rabiu Inusa babban sakatare a ma’aikatar gidaje da bunÆ™asa birane ta jihar Kaduna, shi ne ya bayyana haka ranar Litinin a wurin taron hukumar filaye, gidaje da bunkasa birane ta Æ™asa wanda aka gudanar a jihar.

Yunusa ya ce akwai karancin gidaje a Najeriya sosai kuma gwamnatin jihar Kaduna ta shirya shawo kan lamarin.

Ya ce gwamnan jihar Uba Sani ya na kokarin aiwatar da wani shiri na gina gidaje a faɗin ƙananan hukumomin jihar 23.

Ya kara da cewa tuni gwamnatin jihar ta gayyaci wata kungiyar agaji da ƙasar Qatar inda za su samar da gidaje 500 ga mutane masu karamin karfi.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...