Gwamnatin Filato ta sanya dokar hana fita a Mangu saboda rashin tsaro

Gwamnan jihar Filato Caleb Mutfwang ya kafa dokar hana fita ta sa’o’i 24 a karamar hukumar Mangu sakamakon hare-haren da suka kai ga asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.

A wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Gwamnan, Gyang Bere ya sanya wa hannu, an dau matakin sanya dokar ta-bacin ne bayan tattaunawa da hukumar tsaro ta jihar da nufin maido da doka da oda a cikin al’ummomin da abin ya shafa.

Sakamakon dokar zaman gida, an hana zirga-zirga a cikin karamar hukumar har sai wani lokaci sai jami’an tsaro da masu gudanar da ayyuka masu muhimmanci yayin da aka umarci jami’an tsaro da su aiwatar da cikakken bin umarnin.

Gwamnan ya baiwa ‘yan jihar tabbacin tsaron rayuka da dukiyoyi da kuma dawo da zaman lafiya da tsaro a jihar.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...