

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanya hannu kan wata doka ta musamman da ta sauya fasalin ma’aikatun gwamnatin jihar daga 28 zuwa 16.
A cewar Sulaiman Bala Idris mai magana da yawun gwamnan wanda ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce an dauki matakin ne domin rage barna a gwamnati da kuma kawar da yin aiki iri daya da wasu ma’aikatun ke yi.
Ya ce gwamnan ya rattaba hannu kan dokar ne a dakin taron majalisar zartarwar jihar ranar Alhamis a Gusau.
Sabababbin ma’aikatun da aka amince da su sun haɗa da ma’aikatar: