Gwamnan Zamfara ya rage yawan ma’aikatun jihar zuwa 16 daga 28

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanya hannu kan wata doka ta musamman da ta sauya fasalin ma’aikatun gwamnatin jihar daga 28 zuwa 16.

A cewar Sulaiman Bala Idris mai magana da yawun gwamnan wanda ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce an dauki matakin ne domin rage barna a gwamnati da kuma kawar da yin aiki iri daya da wasu ma’aikatun ke yi.

Ya ce gwamnan ya rattaba hannu kan dokar ne a dakin taron majalisar zartarwar jihar ranar Alhamis a Gusau.

Sabababbin ma’aikatun da aka amince da su sun haɗa da ma’aikatar:

  • Noma
  • Kasafin kudi da tsare-tsare
  • Kimiyya da Fasaha
  • Muhalli da Arzikin ƙasa
  • Kudi
  • Lafiya
  • Kasuwanci
  • Cikiniki da Masana’antu
  • Gidaje da Bunkasa Birane
  • Shari’a
  • Al’adu da Yada Labarai
  • Kananan Hukumomi da Masarautu
  • Addinai
  • Mata da Cigaban Jama’a
  • Matasa da Wasanni
  • Aiyuka da Ababen more rayuwa
  • Tsaro da Harkokin Cikin Gida

More from this stream

Recomended