Gwamnan Kebbi ya sasanta wani rikicin manoma da makiyaya

Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris ya sasanta rikicin manoma da makiyaya a kananan hukumomin Suru da Koke Besse na jihar domin kawo zaman lafiya.

Ya ce tattaunawa ita ce sahiyiyar hanya ɗaya ta magance rikicin manoma da makiyaya a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.

Idris wanda ya garzaya zuwa yankin biyo bayan rikicin manoma da makiyaya da aka yi asarar rayuka biyu a yayin da aka kwantar da wasu takwas a asibiti biyo bayan raunin da suka samu.

Ya bayar da tallafin miliyan 4 ga waÉ—anda suka mutu a yayin da wadanda suka jikkata aka basu tallafin miliyan biyar a karamar hukumar Suru.

A yayin da yake karamar hukumar Besse inda mutane biyu suka ɓata aka kuma kashe mutum ɗaya gwamnan ya gaggauta kwamitin sasantawa ƙarkashin jagorancin kwamishinan ƴan sandan jihar da kuma sauran shugabannin hukumomin tsaro da suka haɗa da DSS da kuma Civil Defence.

More News

Hukumar NMDPRA ta rufe wani gidan mai da ya karkatar da tankar man fetur 18

Hukumar NMDPRA dake lura da tacewa tare rarraba man fetur da iskar gas ta rufe gidan man Botoson Oil and Gas LTD dake jihar...

Jirgin saman kamfanin Xejet ya zame daga kan titin filin jirgin saman Lagos

A ranar Asabar ne wani jirgin sama mallakin kamfanin Xejet ya zame daga kan titin filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos. Hukumar NSIB dake...

Lauya ya nemi kotu ta bashi mako 4 ya nemo inda Yahaya Bello ya É“uya

Abdulwahab Mohammed babban lauyan tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya nemi babbar kotun tarayya dake Abuja da ta bashi makonni huÉ—u domin ya...

ÆŠalibai 9 aka tabbatar da yin garkuwa da su daga jami’an jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa É—alibai 9 aka tabbatar sun É“ace bayan da wasu Æ´an bindiga suka kai farmaki Jami'ar Kimiya da...