Gwamantin Najeriya ta cire malaman jami’o’i daga tsarin biyan albashi na IPPIS

Gwamnatin tarayya ta cire manyan makarantu daga tsarin haɗin gwiwar ma’aikata da tsarin biyan albashi na IPPIS.

Ministan ilimi, Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana hakan a lokacin da yake yi wa manema labarai fadar shugaban kasa bayani tare da wasu ministoci kan sakamakon taron na FEC.

Sannan ya ce hakan zai fara aiki ne cikin gaggawa.

A cewarsa, FEC ta yi la’akari da cewa shugaban jami’o’in ba sa bukatar su bar aikinsu don zuwa Abuja don neman biyan albashin ma’aikatansu.

More from this stream

Recomended