Ganduje ya jagoranci taron shugabannin jam’iyar APC

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma sabon shugaban jam’iyar APC, Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci zaman taron shugabannin jam’iyar na farko.

Taron ya gudana ne a ofishin jam’iyar na kasa dake Abuja.

A ranar 3 ga watan Agusta ne aka zabi, Ganduje a matsayin sabon shugaban jam’iyar a wurin taron kwamitin zartarwar jam’iyar.

Ganduje ya maye gurbin, Abdullahi Adamu wanda ya sauka daga kan mukaminsa na shugabancin jam’iyar a cikin watan Yuli.

More from this stream

Recomended