Ganduje bai damu da binciken bidiyon dala ba—Tsohon Kwamishina

Muhammad Garuba, tsohon kwamishinan yada labarai na jihar Kano a karkashin gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ya ce tsohon gwamnan bai damu da matakin da gwamnatin jihar ta dauka na sake bude binciken faifan bidiyon dala da ke nuna yana karbar cin hanci ba.

Shugaban hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano Barista Muhuyi Magajin Rimin-Gado, ya yi alkawarin sake bude binciken da ake yi wa tsohon gwamnan.

Rimin-Gado ya ce “Kowane gwamna, mataimakin gwamna ko shugaban kasa mai ci yana da kariya, yanzu wannan kariya ta kare, hukumar za ta yi abin da ya kamata.”

Sai dai tsohon kwamishinan yada labarai na jihar, Muhammad Garba, wanda abokin tsohon gwamnan ne, ya bayyana rashin damuwarsu game da lamarin a wata hira da BBC Hausa.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...