FG ta ayyana Laraba da Alhamis a matsayin ranakun hutu

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba, 28 ga watan Yuni da Alhamis 29 ga watan Yuni a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallah Babba.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa daga Oluwatoyin Akinlade, babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida.

Sanarwar ta ce, “Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Laraba 28 ga watan Yuni da Alhamis 29 ga watan Yuni 2023 a matsayin ranakun hutun jama’a domin tunawa da bikin Eid-el-Kabir na bana tare da taya al’ummar Musulmi a gida da kuma kasashen waje.”

“Muna fatan addu’o’i da sadaukarwa da suka zo tare da wannan gagarumin biki, da kuma sakon Eid-el-Kabir, za su kawo zaman lafiya, hadin kai da ci gaba a Najeriya.”

Musulmai a fadin duniya na shirin gudanar da Sallar Eid El-Kabir, wanda aka fi sani da Babbar Sallah a Arewacin Najeriya, ranar Laraba.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...