EFCC ta kama masu sayen kuri’a a zaben gwamna

EFCC ta ce ta cafke mutum 14 a jihohin Imo da Bayelsa da kuma Kogi bisa zargin su da yunĆ™urin sayen Ć™uri’u daga masu zaÉ“e a zaÉ“en gwamnonin jihohin da ya gudana a ranar Asabar.

Hukumar ta ƙwace kuɗi naira miliyan 11,040,000 daga irin waɗannan mutanen.

An kama waÉ—anda ake zargin ne a garin Otueke da Adawari na jihar Bayelsa, da kuma wasu a jihohin Kogi da Imo.

EFCC ta ce ta samu nasarar hakan ne sanadiyyar bayanan sirri da ta tattara tun gabanin ranar gudanar da zaɓukan.

Bugu da ƙari hukumar ta samu nasarar ƙwace motoci biyu daga masu ƙoƙarin aikata laifukan na zaɓe.

Hukumar ta ce za a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala gudanar da bincike a kansu.

A wannan Asabar ɗin ne INEC ta gudanar da zaɓukan gwamnan a jihohin na Kogi da Imo da Bayelsa, zaɓukan da aka samu koke-koke na tashe-tashen hankula da rikice-rikice a yankuna daban-daban.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...