EFCC Ta Gayyaci Betta Edu Kan Badaƙalar Miliyan 585

Hukumar EFCC ta gayyaci, Betta Edu ministar ma’aikatar jin ƙai da kuma yaki da talauci ya zuwa ofishinta domin gudanar da bincike.

Wata majiya dake hukumar ta EFCC ta bayyanawa jaridar The Cable cewa an gayyaci Edu ta bayyana a hukumar da zarar ta samu dama.

“Gwamnati ta umarce mu da mu bincike ta kan badakalar miliyan 585 kuma za muyi haka,” a cewar majiyar.

Tun da farko a ranar Litinin ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bada sanarwar dakatar da ministar daga aiki har sai bayan an kammala bincike kan zargin da ake mata.

Gayyatar da EFCC ke yi wa ministar na zuwa ne kasa da mako guda bayan EFCC ta gayyaci tsohuwar ministar ma’aikatar ta jin ƙai da yaki da talauci Sadiya Umar Faruq kan zargin badaƙalar biliyan 37.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...