Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ta yi Allah wadai da kisan da wasu kungiyoyi dauke da makamai suka yi wa sojojin Nijar.
Sojojin Nijar 17 ne aka kashe a ranar Talata a wani hari da wasu da ake zargin mayakan jihadi ne suka kai a kusa da iyakar kasar da Mali da ke yammacin kasar, in ji ma’aikatar tsaron kasar.
Wani sashen sojojin ne “harin ta’addanci ya rutsa da shi a kusa da garin Koutougu,” in ji ma’aikatar cikin wata sanarwa da yammacin Talata.
Ya kara da cewa wasu sojoji 20 sun jikkata, shida masu tsanani, sannan an kwashe dukkan wadanda suka jikkata zuwa Yamai babban birnin kasar.
Sama da maharan 100 ne aka ɓatar da su, in ji rundunar.
Sai dai a wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, ECOWAS ta nuna damuwa kan kashe-kashen da aka yi wa sojoji a Nijar, yayin da ta nuna juyayi ga iyalan wadanda abin ya shafa.
Sanarwar ta kara da cewa, “ECOWAS ta samu mummunan labarin bakin ciki na hare-hare daban-daban da wasu kungiyoyi masu dauke da makamai suka kai a Jamhuriyar Nijar wadanda suka yi sanadin mutuwar sojojin Nijar da dama.