Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), a ranar Talata, sun kama wasu jami’an Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar da ke karkatar da kayayyakin tallafin jama’a da ake yi wa ‘yan kasa don dakile raɗaɗin cire tallafin man fetur.
Wasu daga cikin wadanda ake zargin da aka kama a wata shahararriyar kasuwa da ke garin Lafia, babban birnin jihar Nasarawa inda ake sayar da kayayyakin sun hada da jami’an hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Nasarawa (NASEMA) da sauran abokan aikinsu.
Kakakin rundunar ‘yan sandan sirri, Peter Afunanya, wanda ya bayyana wa manema labarai ci labarin a Abuja, ya bayyana cewa an kwato wasu daga cikin kayayyakin da aka karkatar daga hannun wadanda ake zargin.
Afunanya ya yi kira ga jama’a da ke da bayanan da suka shafi al’amuran da suka kunno kai da su kai rahoto ga jami’an tsaro da abin ya shafa domin daukar matakin da ya dace, yana mai cewa za a hukunta masu laifin kamar yadda doka ta tanada.
“Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta samu rahotanni daga wasu Gwamnonin Jihohin da suka shafi karkata ko sayar da kayan abinci da ake da niyyar ba wa ‘yan kasa.
“Saboda haka, hukumar ta gudanar da bincike a kan haka kuma ta gano wasu daga cikin kayayyakin tare da kama wadanda ake zargin,” in ji kakakin DSS.
Ya kara da cewa yayin da suke ci gaba da gudanar da ayyukansu a wasu jihohin, tuni hukumar ta kama wani da ake zargi da aikata laifuka a jihar Nasarawa da ke da hannu wajen karkatar da kayan abinci da kuma sayar da kayan agajin da aka tanadar wa masu karamin karfi a wurin.