Daliban Najeriya Sun Bayyana Farin Cikin Su Kan Kwaso Su Daga Sudan

Mintoci kaɗan bayan saukar su a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja kaso na farko na yan Najeriya da aka kwaso daga Sudan sun bayyana farin cikin su da dawowa gida.

Mutanen da aka kwaso mafi yawancin su da aka kwaso ɗalibai ne dake karatu a kasar ta Sudan.

Jirgin saman sojan Najeriya samfurin C-130H da kuma na kamfanin jiragen saman Air Peace su ne suka dawo ɗaliban.

“Nayi matukar farin ciki da na dawo gida” a cewar wata daliba

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]