Cutar Anthrax:Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargadi Akan Cin Ganda

Gwamnatin tarayya ta fitar da wani gargadi kan barkewar cutar anthrax a wasu daga cikin kasashe makota da kuma cin ganda.

A wata sanarwa ranar Litinin,Ernest Umakhihe babban sakataren ma’aikatar gona ya ce cutar ta halaka rayukan mutane a arewacin Ghana dake da iyaka da Togo da Burkina Faso.

Cutar Anthrax wata cuta ce nau’in Bacteria dake kama dabbobi masu cin ciyawa irin su shanu, akuya da kuma tinkiya.

Mutane za su iya kamuwa da cutar idan suka yi mu’amala da dabbobi masu É—auke da ita ko kuma naman dabbobin.

Amma kuma cutar ta Anthrax bata yaÉ—uwa daga mutum zuwa mutum.

Alamomin cutar sun haɗa da tari, zazzaɓi da kuma ciwon jiki rashin ganowa tare da yin maganinta ka iya kai wa ga mutuwa.

Umakhihe ya ce dabbobin da ba a yi musu riga-kafi ba kuma suke ɗauke da cutar to kuwa cikin sauki za su iya yaɗawa mutum ta hanyar shakar ƙwayoyin cutar ko cin naman dabbar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]