Cutar Anthra ta bulla a Najeriya—Gwamnati

A ranar Litinin ne gwamnatin tarayya ta tabbatar da bullar cutar anthrax a Najeriya, inda ta bayyana cewa an gano cutar a wata gona da ke jihar Neja.

A ranar 13 ga watan Yuni, 2023, jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, gwamnatin tarayya ta sanar da jama’a game da barkewar cutar anthrax a wasu kasashen da ke makwabtaka da yankin Afirka ta Yamma, ta kuma shawarci ‘yan Najeriya da su daina cin ganda, wanda aka fi sani da ponmo.

Gwamnatin kasar ta bayyana musamman cewa cutar ta yadu a arewacin Ghana mai iyaka da Burkina Faso da Togo, kamar yadda ta kuma yi alkawarin ci gaba da sanar da ‘yan Najeriya bayanai game da cutar.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya ta fitar a Abuja ranar Litinin, ta ce ta damu matuka da sanar da tabbatar da bullar cutar anthrax a jihar Neja ta Najeriya.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...