Cutar Anthra ta bulla a Najeriya—Gwamnati

A ranar Litinin ne gwamnatin tarayya ta tabbatar da bullar cutar anthrax a Najeriya, inda ta bayyana cewa an gano cutar a wata gona da ke jihar Neja.

A ranar 13 ga watan Yuni, 2023, jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, gwamnatin tarayya ta sanar da jama’a game da barkewar cutar anthrax a wasu kasashen da ke makwabtaka da yankin Afirka ta Yamma, ta kuma shawarci ‘yan Najeriya da su daina cin ganda, wanda aka fi sani da ponmo.

Gwamnatin kasar ta bayyana musamman cewa cutar ta yadu a arewacin Ghana mai iyaka da Burkina Faso da Togo, kamar yadda ta kuma yi alkawarin ci gaba da sanar da ‘yan Najeriya bayanai game da cutar.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya ta fitar a Abuja ranar Litinin, ta ce ta damu matuka da sanar da tabbatar da bullar cutar anthrax a jihar Neja ta Najeriya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]