Bankin Duniya ya yi hasashen cewa za a samu raguwar kudaden da mutane ke aika wa gida daga kasshen duniya da kashi 20 cikin 100 a wannan shekarar, yayin da ake fuskantar matsalar tattalin arziki da kuma rufe harkokin kasuwanci a duniya saboda cutar korona.
Wannan shi ne babban koma bayan da aka fuskanta kan abin da aka kira madogarar rayuwar mutane da dama a Afrika da kuma sauran nahiyoyi.
‘Yan ci rani da yawa ba za su samu damar aikewa da kudade gida ba saboda ayyukansu da kuma abin da ake biyansu na cikin halin rashin tabbas.
Kudaden da ma’aikata daga kasashen waje a duniya ke aikewa gida kasashensu, an yi hasashen za su ragu da kusan dala biliyan 445.
Hasashen ya ce za a samu raguwar ne a kasashen Kudu da Hamadar Sahara da kashi 23 cikin 100 wanda yawan kudin zai kai dala biyan 37 a wannan shekarar.
Ga taswirorin da ke nuna yadda lamarin yake: