Coronavirus: Majalisar dokoki za ta binciki ‘yan China da aka shigo da su Najeriya

Majalisar Wakilan Najeriya ta kaddamar da bincike game da wasu ‘yan kasar China da gwamnati ta kai kasar a watan jiya da sunan taimaka wa bangaren kiwon lafiya wajen yaki da annobar korona.

A baya-bayan nan dai ana ta ce-ce-ku-ce a kasar kan ‘yan kasar ta China musamman bayan da aka daina jin duriyarsu da kuma sanin aikin da suke yi a cikin Najeriya.

Wasu rahotanni a kasar ma na cewa wasu daga cikin ‘yan Chinar, ma’aikatan gine-gine ne ba likitoci ba, kuma hatta jami’an da ke yaki da cutar ta korona ba su da cikakkiyar masaniyar inda suke.

A cewar Honourable Abdulrazak Namdas, irin wadannan ce-ce-ku-cen da ake yi na daya daga cikin wannan na cikin dalilan da yasa majalisar wakilan kasar ta kaddamar da bincike domin gano gaskiyar al’amarin.

Namdas ya bayyana cewa tun bayan shigar ‘yan Chinar Najeriya, ba su sake jin labarinsu ba kuma ga shi cuta na Æ™ara yaÉ—uwa.

Ya bayyana cewa a wannan dalili ne ya sa majalisa ta ce da farko yakamata a gano a ina ‘yan Chinar suke? Da kuma ainahin me ya kawo su?

Ya bayyana cewa “‘yan Najeriya na da ‘yancin su san a ina mutanen nan suke don mu san sun zo da cuta ne ko ba su da shi.”

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da Æ´an ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an Æ´an sanda da kuma sojoji suna É—aukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar Æ´an sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe É—an Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa HaÉ—in Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...