Coronavirus: Majalisar dokoki za ta binciki ‘yan China da aka shigo da su Najeriya

Majalisar Wakilan Najeriya ta kaddamar da bincike game da wasu ‘yan kasar China da gwamnati ta kai kasar a watan jiya da sunan taimaka wa bangaren kiwon lafiya wajen yaki da annobar korona.

A baya-bayan nan dai ana ta ce-ce-ku-ce a kasar kan ‘yan kasar ta China musamman bayan da aka daina jin duriyarsu da kuma sanin aikin da suke yi a cikin Najeriya.

Wasu rahotanni a kasar ma na cewa wasu daga cikin ‘yan Chinar, ma’aikatan gine-gine ne ba likitoci ba, kuma hatta jami’an da ke yaki da cutar ta korona ba su da cikakkiyar masaniyar inda suke.

A cewar Honourable Abdulrazak Namdas, irin wadannan ce-ce-ku-cen da ake yi na daya daga cikin wannan na cikin dalilan da yasa majalisar wakilan kasar ta kaddamar da bincike domin gano gaskiyar al’amarin.

Namdas ya bayyana cewa tun bayan shigar ‘yan Chinar Najeriya, ba su sake jin labarinsu ba kuma ga shi cuta na Æ™ara yaÉ—uwa.

Ya bayyana cewa a wannan dalili ne ya sa majalisa ta ce da farko yakamata a gano a ina ‘yan Chinar suke? Da kuma ainahin me ya kawo su?

Ya bayyana cewa “‘yan Najeriya na da ‘yancin su san a ina mutanen nan suke don mu san sun zo da cuta ne ko ba su da shi.”

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...