China ta yi ramuwa kan rufe mata ofishin jakadanci a Amurka

The US Consulate-General in Chengdu is pictured on July 23, 2020 in Chengdu, Sichuan Province of China.

Bayanan hoto,
Ofishin jakadancin Amurka na Chengdu

China ta mayar da martani kan rikicin diflomasiyyarta da Amurka wanda ke Æ™ara ta’azzara.

Mahukuntan Beijing dai sun buƙaci Amurka ta rufe ofishin jakadancinta da ke Chengdu, a kudancin ƙasar.

China dai ta bayyana al’amarin a matsayin halartaccen mataki da ya zama dole.

A wani abu mai kama da idan ka ce kule zan ce ma cas, yanzu dai China ta mayar da martani kan rufe ofishin jakadancinta da Amurka ta ba da umarni a Houston.

China dai ta buƙaci ita ma Amurka ta rufe nata ƙaramin ofishin jakadancin da ke tsakiyar lardin Sichuan na kudancin ƙasar.

Tun a tsakiyar 1980 ne, Amurka ta buÉ—e ofishin jakadancin na Chengdu.

Daga cikin ayyukansa akwai lura da ayyukan sa-idon gwamnatin Amurka da kuma dangantakarta da yankin Tibet, wanda tsawon lokaci ke fafutuka don ganin hukumomin China sun ba shi Æ™arin ‘yanci.

Matakin na zuwa ne bayan Amurka ta umarci China ta rufe ƙaramin ofishin jakadancinta da ke Houston, inda ta yi iƙirarin cewa matakin yunƙuri ne na kare sirrin Amurkawa da haƙƙin mallakar ƙirƙire-ƙirƙirensu.

China dai ta bayyana matakin a matsayin wani gagarumin keta dokar ƙasashen duniya.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da Æ´an ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an Æ´an sanda da kuma sojoji suna É—aukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar Æ´an sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe É—an Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa HaÉ—in Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...