Chelsea ta koma ta uku a teburin Premier League

Olivier Giroud scores for Chelsea against Crystal Palace

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Giroud ne ya fara ci wa Chelsea kwallo kuma na uku kenan da ya zura a raga tun da aka ci gaba da wasannin Premier League

Chelsea ta doke Crystal Palace da ci 3-2 a wasan mako na 34 a gasar Premier League da suka fafata ranar Talata a Selhust Park ta kuma koma ta uku a teburi.

Chelsea ce ta fara cin kwallo a minti na shida da fara wasa ta hannun Olivier Giroud, sannan Christian Pulisic ya kara na biyu.

Daga nan Palace ta zare kwallo daya ta hannun Wilfried Zaha, kuma haka suka je hutu Chelsea ta ci biyu ita kuwa Palace da daya a raga.

Bayan da aka ci gaba da karawar zagaye na biyu ne Chelsea ta kara na uku ta hannun Tammy Abraham wanda ya shiga karawar daga baya.

Sai dai minti daya tsakani da Chelsea ta ci kwallo na uku ne, Christian Benteke ya zare daya.

Nasarar da Chelsea ta yi ya sa ta koma ta uku a teburin Premier League da tazarar maki biyu tsakaninta da Leicester City wacce ta koma ta hudu.

Leicester za ta ziyarci Arsenal a daya wasan mako na 34 da za su kece raini a gasar ta cin kofin Premier League wacce tuni Liverpool ta cinye kofin bana.

Crystal Palace mai maki 42 tana ta 14 a kasan teburin shekarar nan, kuma ta yi rashin nasara a wasa hudu a jere.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...