Chelsea ta koma ta uku a teburin Premier League

Olivier Giroud scores for Chelsea against Crystal Palace

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Giroud ne ya fara ci wa Chelsea kwallo kuma na uku kenan da ya zura a raga tun da aka ci gaba da wasannin Premier League

Chelsea ta doke Crystal Palace da ci 3-2 a wasan mako na 34 a gasar Premier League da suka fafata ranar Talata a Selhust Park ta kuma koma ta uku a teburi.

Chelsea ce ta fara cin kwallo a minti na shida da fara wasa ta hannun Olivier Giroud, sannan Christian Pulisic ya kara na biyu.

Daga nan Palace ta zare kwallo daya ta hannun Wilfried Zaha, kuma haka suka je hutu Chelsea ta ci biyu ita kuwa Palace da daya a raga.

Bayan da aka ci gaba da karawar zagaye na biyu ne Chelsea ta kara na uku ta hannun Tammy Abraham wanda ya shiga karawar daga baya.

Sai dai minti daya tsakani da Chelsea ta ci kwallo na uku ne, Christian Benteke ya zare daya.

Nasarar da Chelsea ta yi ya sa ta koma ta uku a teburin Premier League da tazarar maki biyu tsakaninta da Leicester City wacce ta koma ta hudu.

Leicester za ta ziyarci Arsenal a daya wasan mako na 34 da za su kece raini a gasar ta cin kofin Premier League wacce tuni Liverpool ta cinye kofin bana.

Crystal Palace mai maki 42 tana ta 14 a kasan teburin shekarar nan, kuma ta yi rashin nasara a wasa hudu a jere.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...