Shugaban mulkin soja na kasar Burkina Faso yasa ka hannu kan wata yarjejeniya da kasar Rasha ta gina tashar wutar lantarki ta makamashin nukiliya domin inganta samar da wutar lantarki a ƙasar.
Saka hannun na zuwa ne biyo bayan tattaunawa tsakanin Ibrahim Traore da shugaban kasar Russia Vladimir Putin a cikin watan Yuni a wurin taron kasashen Africa-Russia.
A wurin taron Traore ya roki ƙasar Rasha da ta gina tashar wutar lantarki ta nukiliya a kasar Burkina Faso wanda ya ce za ta taimaka wajen samar da wutar da kasar ke bukata.
Traore ya ƙwaci mulki ne a watan Satumba na shekarar 2022 kuma tuni ya mayar da hankali wajen kulla alaka da kasar Rasha domin samun tallafin tsaro da kuma na tattalin arziki.