Shugaban kasa, Muhammad Buhari ya dawo gida Najeriya bayan ziyarar da ya kai kasar Koriya ta Kudu.
Buhari ya kai ziyarar ne domin halartar taron riga kafi na duniya.
A yayin ziyarar shugaban kasar ya gana da tsohon shugaban Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki Moon.
Har ila yau shugaban kasar ya sanya idanu kan yarjejeniyar da aka kulla ta gyara matatar man fetur dake Kaduna.