Buhari: Shettima ba zai bawa yan Najeriya kunya ba

Shugaban kasa, Muhammad Buhari ya ce dan takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar APC, Kashim Shettima ba zai bawa Najeriya kunya ba idan jam’iyar ta ci zaben shekarar 2023.

Buhari ya fadi haka ne a ranar Juma’a lokacin da yake ganawa da wasu jiga-jigan jam’iyar APC a fadar Aso Rock.

Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na kasa, shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan, Atiku Bagudu gwamnan jihar Kebbi da mataimakin shugaban majalisar wakilai, Idris Wase na daga cikin wadanda suka halarci taron.

A cewar wata sanarwa da Femi Adesina ya fitar Buhari ya ce tsohon gwamnan jihar Borno ” Ba zai bawa yan Najeriya kunya ba”.

Shugaban kasar ya kuma ya ba musu kan yadda suka taimaka aka yi babban taron jam’iyyar lafiya da kuma zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyar.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...