BBC Hausa: Bola Tinubu ya lashe zaben shugaban Najeriya na 2023

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya sanar da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2023 da kuri’a miliyan 8,794,726.

Tsohon matainmakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ne ke biye masa da kuri’u miliyan 6,984,520.

Sai kuma dan takarar jam’iyyar Labour, Peter Obi wanda ya samu kuri’a miliyan 6,101,533.

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya zo na hudu da kuri’u miliyan 1,496,687.

Idan an jima ne kuma mutumin da ya yi nasarar wato Bola Ahmed Tinubu zai je dakin taron da ake tattara sakamako domin karbar shaidar lashe zaben.

Kusan za a iya cewa wannan ne sakamakon zaben da ya fi kowanne daukar dogon lokacin kafin a sanar da shi a baya-bayan nan sakamakon dalilai da dama.

Jam’iyyun adawa na PDP da LP sun ce ba za su karbi sakamakon ba bisa zargin tafka magudi a mazabu da dama, inda kuma suka ce za su garzaya kotu.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...