Bayan fitowa daga gidan yarin Joshua Dariye na shirin tsayawa takarar sanata

Matukar ba a samu sauyi daga baya ba to kuwa tsohon gwamnan jihar Filato, Joshua Dariye zai ayyana aniyarsa ta tsayawa takarar majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Filato ta Tsakiya a karkashin jam’iyyar LP.

Dariye da kuma tsohon gwamnan jihar Taraba, Joly Nyame na daga cikin waɗanda aka saka daga gidan yarin Kuje watanni uku bayan da majalisar kolin ƙasa da shugaban kasa, Buhari yake jagoranta tayi musu afuwa.

Bayanan da jaridar Daily Trust ta tattara sun nuna cewa jam’iyyar LP reshen jihar Filato ta kammala shirye-shiryen tarbar tsohon gwamnan daga Abuja domin ta bashi fom din takara.

Wani jami’i a jam’iyar ta Labour Party da ya bukaci a boye sunansa ya fadawa jaridar cewa tabbas suna shirye-shiryen zuwan Dariye domin yazo ya ayyana takararsa kuma suna da yakinin zai bada mamaki.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...