Batutuwan Da Shugabannin ECOWAS Za Su Tattauna Akai

VOA Hausa

Batun takardar kudadin bai daya wato ECO da ya kamata a soma amfani da ita a wannan shekara ta 2020 na daga cikin mahimman batutuwan da shuwagabanin kasashen ECOWAS ke tantaunawa akansu.

Za su duba hanyoyin warware daurin kan dake tattare da wannan shiri bayan da kasashen Afrika ta yamma renon Faransa suka ayyana yunkurin soma amfani da kudin na ECO duk kuwa da cewa ainihi CEDEAO ke da wannan kudiri inji shugaban kasar Nijar Issouhou Mahamadou mai masaukin baki.

ECOWAS
ECOWAS

Taron wanda ke gudana a dai dai lokacin da shugaba Issouhou Mahamadou ke kammala wa’adin shugabancin kungiyar ta ECOWAS zai saurari shawarwari daga bakin shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya a game da matakan yaki da cutar coronavirus a matsayinsa na gwarzon yaki da wannan anoba a yankin Afrika ta yamma.

Kana za su tattauna kan yanayin da ake ciki a kasar Mali bayan juyin mulkin da ya kawarda Ibrahim Boubacar Keita daga karagar mulki.

Daga bison wannan zama zai dubi sha’anin tsaro a wannan yanki wanda ke ci gaba da tabarbarewa.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...