Basaraken gargajiya ya mutu a Lagos bayan Sallar Idi

Kabiru Agbabiaka Osolo na Isolo dake jihar Lagos ya rasu.

Basaraken na jihar Lagos ya rasu ne da safiyar ranar Laraba.

A wata sanarwa Olasoju Adebayo shugaban ƙaramar hukumar mulki ta Isolo ya ce an gudanar da jana’izar marigayin a ranar Laraba da ƙarfe 4 na yamma.

“Yana da shekaru 64 za ayi jana’izarsa yau ƙarfe 4 a fadarsa dake layin Akinbaye Isolo kamar yadda addinin musulunci ya tanada,” a cewar sanarwar.

Shugaban ƙaramar hukumar bai bayyana dalilin mutuwar marigayin ba sai dai wasu majiyoyi sun bayyana marigayin ya halarci Sallar Idin ƙaramar sallah da aka yi a ranar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]