Babban Sifetan Yan Sanda Ya Kai Ziyara Jihar Filato Mai Fama Da Rikici

Babban Sifetan Yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya ziyarci birnin Jos a ranar Juma’a kan hare haren da aka kai wasu kauyukan jihar a yan kwanakin nan.

Sama da mutane 150 ne aka kashe a wasu garuruwa 17 dake kananan hukumomin Bokkos, Barikin Ladi da kuma Mangu gabanin bikin Kirisimeti.

Gidaje da dama maharan suka kona abun da ya tilastawa mazauna gidajen zama yan gudun hijira.

Biyo bayan faruwar lamarin gwamnatin tarayya ta yi wa mutanen da abun ya shafa alkawarin bin kadin hakkinsu.

A yayin ziyarar, Egbetokun ya gana da gwamnan jihar, Caleb Mutfwang da kuma sauran masu ruwa da tsaki a jihar.

Ya kuma bada umarnin gaggawa ga mataimakin babban sifetan yan sanda mai kula da shiya ta 4 da ya tattara ya koma jihar da zama ba tare da bata lokaci.

More News

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu É“atagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an Æ´an sanda da haÉ—in gwiwar Æ´an bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...

Jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari a Akwa Ibom

Wasu ma'aikatan kamfanin haƙar man fetur su 6 da kuma matuƙan jirgi su biyu su mutu a wani hatsarin jirgi mai saukar ungulu a...

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...