Ba ni da niyyar barazana wa kowa – Gwamna Ganduje

Dakta Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan Jihar Kano, ya yi alkawarin shugabanci nagartacce cewa Bazan yaudari mutanen jihar ba kuma babu wanda gwamnatina zata tozarta ko kuma ta razana

A wata sanarwa dauke dasa hannun kwamishinan bayanai na jihar Muhammad Garba, gwamnan ya bayyana cewa gwamnatinsa bata da kudirin kulla makirci ga kowa imma a matakin gwamnati ko kuma a wani mataki na mai zaman kansa

Bamu da kudirin tozarta kowa imma ma’aikacin gwamnati ko wani mai zaman kansa

Zabe ya kunshi zafafan muhawara kan banbancin akidar siyasa amma duk sun zama tarihi sannan muna da babban aiki a gabanmu na hada kai muyi aiki tare saboda Kano mallakarmu ce dukka

Yace nasarar gwamnan a zaben jihar mallakar dukkanin mutane ne ba tare da la’akari da banbancin akidar siyasa ba don haka tare za muyi aiki domin cigaban jihar

Za mu rungumi kwa; sarakunan gargajiya, malamai, ma’aikatan gwamnati da duk sauran jam’iyyar da ke da muradi. Akwai bukatar mu hadu da dukkanin mutane don cigaban jiharmu

Yace Ganduje zai cigaba da kasancewa a matsayarsa na mutunta duk wadanda suka cancanta, cewa gwamnan zai mika hannu ga duk wanda yazo sannan yayi aiki tare da kowa
domin cigaban jihar

Inda a karshe yayi addu’ar Allah ya ganar da masu hassada su gane gaskiya domin cigaban Al’ummar mu

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...