Dakta Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan Jihar Kano, ya yi alkawarin shugabanci nagartacce cewa Bazan yaudari mutanen jihar ba kuma babu wanda gwamnatina zata tozarta ko kuma ta razana
A wata sanarwa dauke dasa hannun kwamishinan bayanai na jihar Muhammad Garba, gwamnan ya bayyana cewa gwamnatinsa bata da kudirin kulla makirci ga kowa imma a matakin gwamnati ko kuma a wani mataki na mai zaman kansa
Bamu da kudirin tozarta kowa imma ma’aikacin gwamnati ko wani mai zaman kansa
Zabe ya kunshi zafafan muhawara kan banbancin akidar siyasa amma duk sun zama tarihi sannan muna da babban aiki a gabanmu na hada kai muyi aiki tare saboda Kano mallakarmu ce dukka
Yace nasarar gwamnan a zaben jihar mallakar dukkanin mutane ne ba tare da la’akari da banbancin akidar siyasa ba don haka tare za muyi aiki domin cigaban jihar
Za mu rungumi kwa; sarakunan gargajiya, malamai, ma’aikatan gwamnati da duk sauran jam’iyyar da ke da muradi. Akwai bukatar mu hadu da dukkanin mutane don cigaban jiharmu
Yace Ganduje zai cigaba da kasancewa a matsayarsa na mutunta duk wadanda suka cancanta, cewa gwamnan zai mika hannu ga duk wanda yazo sannan yayi aiki tare da kowa
domin cigaban jihar
Inda a karshe yayi addu’ar Allah ya ganar da masu hassada su gane gaskiya domin cigaban Al’ummar mu