Tsohon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya musanta wasu raÉ—e-raÉ—i da ke yawo da ke bayyana cewa yana tattaunawa da gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje don yin sulhu.
Yayin wata hira da Channels TV da yammacin ranar Lahadi. Kwankwaso ya ce ya ji daÉ—in ziyarar ta’aziyyar da Ganduje ya kai masa kwanakin baya, amma bayan wannan ziyara ta gaisuwa babu wata magana da ake yi a bayan fage dangane da yin sasantawa.
Ya bayyana yadda alaƙarsa ta kasance da Gandujen a baya tun lokacin da ya yi mata mataimakin gwamnan Kano a zaɓen 1999, da kuma yadda suka ci gaba da aiki tare har zuwa 2015 lokacin da suka raba garin bayan ya zama gwamna.
An tambaye shi cewa to shin yanzu idan ka samu wata dama za ka sake bayar da sunan Ganduje kamar yadda ka yi a baya ?.
Sai ya kada baki ya ce ”A yanzu dai ka san ba a jam’iyya É—aya muke ba, don haka ina ga babu ma buÆ™atar yin wannan tambaya, don haka ko da dama ta samu akwai mutanen da suka cancanta cikin waÉ—anda nake tare da su”.
AlaÆ™a tsakanin shugabannin biyu ta daÉ—e da lalacewa tun bayan da Kwankwaso ya miÆ™a wa Ganduje ragamar mulkin Kano a 2015 bayan sun shafe shekara takwas a matsayin gwamna da mataimaki. har ta kai ga yanzu Kwankwaso ya koma jam’iyyar adawa ta PDP.
Sai dai Gwamna Ganduje na ci gaba da fuskantar rikicin cikin gida a jam’iyyarsu ta APC tsakaninsa tawagar tsohon gwamna kuma sanata a yanzu, Malam Ibrahim Shekarau.
Rikicin siyasar Kano dai na ci gaba da kankama musamman a jam’iyyar APC mai mulki, inda tsagin tsohon gwamnan jihar Malam Ibrahim Shekarau ke rikici da É“angaren Ganduje kan shugabancin jam’iyya.
Haka ma a PDP har yanzu tana ƙasa tana dabo tsakanin ɓangaren Kwankwaso da na tsohon ministan harkokin wajen Najeriya Ambasada Aminu Wali, wanda shima ɓangarensa ke adawa da jagorancin Kwankwaso.