Atiku Abubakar ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyar PDP a zaɓen da ya wuce zai yi taron manema labarai a ranar Alhamis 5 ga watan Oktoba.
Dele Momodu wanda shi ne daraktan yaɗa labarai na kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyar PDP shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar.
Dele ya bayyana cewa za a yaɗa ganawar kai tsaye ta shafukan sada zumunta na Atiku da kuma gidajen yaɗa labarai na gida da waje.
Duk da cewa ba a bayyana dalilin ganawa da ƴan jaridun ba ana ganin za ta fi mai da hankali kan batun shari’ar zaɓen shugaban ƙasa dake gaban kotun ƙoli da kuma batun takardun karatun shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.