An yi garkuwa da wasu fasinjoji 15 a jihar Taraba

Fasinjoji 15 aka yi awon gaba da su inda aka tasa ƙeyarsu ya zuwa cikin daji dake tsakanin garin Donga-Maraban Baissa dake ƙaramar hukumar Donga ta jihar Taraba a ranar Litinin.

Fasinjojin da suka haɗa da mata da ƙananan yara na kan hanyarsu ta dawowa daga Zaki-Biam a jihar Benue ya zuwa garin Maihula dake ƙaramar hukumar Bali lokacin da suka Afkawa shingen masu garkuwa da mutanen.

Wasu daga cikin fasinjojin ciki har da direban motar sun samu nasarar tserewa ya zuwa cikin daji inda suka yi tafiyar kusan kilomita 100 a ƙafa kafin su isa garin mai hula.

Musa Tanko wani mazaunin Maihula ya faÉ—awa jaridar Daily Trust cewa dukkanin fasinjojin mazauna garin Maihula ne kuma suna kan hanyarsu ne ta komawa Maihula daga Zaki-Biam inda suka faÉ—a shingen da masu garkuwa da mutane suka saka a wani daji dake Maraban Baissa.

Ƙoƙarin da jaridar Daily Trust ta yi na jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar ya ci tura.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...