An yi garkuwa da mutane a Bauchi

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu mutane biyu a yankin Gumau da ke karamar hukumar Toro a jihar Bauchi.

An ce ‘yan bindigar sun yi harbin iska ne don tsorata mazauna yankin kafin su tafi da wadanda abin ya shafa a safiyar ranar Asabar.

Da yake mayar da martani kan lamarin, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Toro a majalisar wakilai, Hon Dabo Ismail Haruna, ya yi Allah wadai da sace sacen da aka yi kwanan nan.

Ya ce ‘yan bindigar sun dawo suna addabar al’umma ta hanyar yin garkuwa da su ba tare da kakkautawa ba domin neman kudin fansa bayan wani lokaci.Sai dai ya ba wa ‘yan mazaɓar tasa tabbacin shiga tsakani na ‘yan majalisu da za su kawo karshen abubuwan da ba su dace ba, ya kara da cewa yawaitar sace-sacen jama’a a mazabar tarayya ta Toro ya haifar da damuwa sosai a jihar.

Haruna ya yi kira ga gwamnan jihar Sen. Bala Mohammed da gwamnatin tarayya da su gaggauta tura karin jami’an tsaro zuwa karamar hukumar domin kamo miyagu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Ahmed Wakili, bai amsa sakonni ba da kuma kiran da aka yi masa domin tabbatar da faruwar lamarin kafin ya rubuta wannan rahoto.

Sai dai ya ba wa ‘yan mazaɓar tasa tabbacin shiga tsakani na ‘yan majalisu da za su kawo karshen abubuwan da ba su dace ba, ya kara da cewa yawaitar sace-sacen jama’a a mazabar tarayya ta Toro ya haifar da damuwa sosai a jihar.

Haruna ya yi kira ga gwamnan jihar Sen. Bala Mohammed da gwamnatin tarayya da su gaggauta tura karin jami’an tsaro zuwa karamar hukumar domin kamo miyagu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Ahmed Wakili, bai amsa sakonni ba da kuma kiran da aka yi masa domin tabbatar da faruwar lamarin kafin rubuta wannan rahoto.

More News

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...