An yi garkuwa da mutane 40 a lokacin da suke ibada a coci

Akalla mutane 40 ne aka ruwaito a ranar Lahadin da ta gabata cewa wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su a yayin da suke gudanar da taro a cocin Bege Baptist dake Madala a karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna.

Shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya reshen jihar Kaduna, Rabaran John Hayab, ne ya bayyana lamarin a ranar Litinin.

A cewar Hayab, lamarin ya faru ne da karfe 9:30 na safe, a lokacin da ake gudanar da ibada.

An ambato shi yana cewa, “Masu ibadar suna cikin hidimar Lahadi a cikin Cocin sai da misalin karfe 9:30 na safe suka ji karar harbe-harbe a kusa da Cocin. ‘Yan bindigar sun kai hari Cocin kuma suka tafi tare da masu ibada 40.”

Sai dai ya kara da cewa 15 daga cikin masu ibadar da aka yi garkuwa da su sun yi nasarar tserewa, inda suka bar wasu 25 a maboyar masu garkuwar.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...