An tura wani mutum gidan yari bayan da ya ɗirkawa yarinya  ƴar shekara 11 ciki

Wata kotun majistire dake Ikeja a jihar Lagos ta tasa keyar Muyiwa Shonibare mai shekaru 42 ya zuwa gidan yari bayan da aka zarge shi da yin lalata tare da yiwa wata yarinya ƴar shekara 11 ciki.

Alƙaliyar kotun mai shari’a,E. Kubeinje ta umarci jami’an ƴan sanda da su miƙa takardun ƙarar ofishin babban mai shigar da ƙara na jihar domin ya bada shawararsa kana ta dage shari’ar ya zuwa ranar 24 ga watan Afrilu.

Tun da farko ƴan sanda na tuhumar Shonibare wanda yake zaune a layin Odeyele a unguwar Agode Egbe dake yankin Ikotun  a jihar ta Lagos da laifin fyaɗe.

Mai gabatar da ƙara, SP Kehinde Ajayi ya faɗawa kotun cewa Shonibare ya aikata laifin tsakanin watan Agusta zuwa Nuwamban shekarar 2023.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...