An Samu Karin Mutum 663 Da Suka Kamu Da COVID-19 a Najeriya | VOA Hausa

Sabbin alkaluman da hukumar dakile cututtuka ta Najeriya, NCDC ta fitar sun bayyana cewa karin daruruwan mutane sun kamu da cutar COVID-19.

A cewar hukumar, mutum 663 ne cutar ta harba wanda hakan ya mayar da adadin mutanen da suka kamu da cutar zuwa 13,464 a kasar.

Har yanzu dai jihar Legas ce ke kan gaba wajen yawan wadanda ke dauke da cutar, inda yanzu ta sake samun sabbin kamu 170. Sai jihar Ogun da ke bin ta da mutum 108.

Sauran jihohin da aka samu karin wadanda suka kamu da cutar sun hada da Bauchi inda aka samu 69, 49 a Ebonyi, 33 a Edo, 30 a Rivers, 26 a birnin tarayya Abuja, 26 a Jigawa, 20 a Delta, 17 a Anambra, 16 a Gombe, 16 a Kano, 15 a Imo, 14 a Abia, 11 a Borno, 11 a Oyo, 8 a Filato, 6 a Kebbi, 6 a Kaduna, 4 a Ondo, 2 a Naija, 2 a Katsina, 1 a Osun, 1 a Ekiti, 1 a Kwara, 1 a Nasarawa.

Hukumar ta kuma bayyana cewa mutum 4,206 suka warke daga cutar yayin da mutum 365 suka mutu.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...