An Samu Karin Mutum 663 Da Suka Kamu Da COVID-19 a Najeriya | VOA Hausa

Sabbin alkaluman da hukumar dakile cututtuka ta Najeriya, NCDC ta fitar sun bayyana cewa karin daruruwan mutane sun kamu da cutar COVID-19.

A cewar hukumar, mutum 663 ne cutar ta harba wanda hakan ya mayar da adadin mutanen da suka kamu da cutar zuwa 13,464 a kasar.

Har yanzu dai jihar Legas ce ke kan gaba wajen yawan wadanda ke dauke da cutar, inda yanzu ta sake samun sabbin kamu 170. Sai jihar Ogun da ke bin ta da mutum 108.

Sauran jihohin da aka samu karin wadanda suka kamu da cutar sun hada da Bauchi inda aka samu 69, 49 a Ebonyi, 33 a Edo, 30 a Rivers, 26 a birnin tarayya Abuja, 26 a Jigawa, 20 a Delta, 17 a Anambra, 16 a Gombe, 16 a Kano, 15 a Imo, 14 a Abia, 11 a Borno, 11 a Oyo, 8 a Filato, 6 a Kebbi, 6 a Kaduna, 4 a Ondo, 2 a Naija, 2 a Katsina, 1 a Osun, 1 a Ekiti, 1 a Kwara, 1 a Nasarawa.

Hukumar ta kuma bayyana cewa mutum 4,206 suka warke daga cutar yayin da mutum 365 suka mutu.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...