An kori sojojin da suka kashe wani jami’in NDLEA a Neja

Rundunar sojin Najeriya ta gurfanar tare da korar wasu sojoji shida da ake zargi da hannu a mutuwar wani jami’in hukumar NDLEA, Kingsley Chimetalo, a gaban kotu.

An mika hudu daga cikin sojojin da abin ya shafa ga ‘yan sanda yayin da biyu suka gudu. 

Sojojin hudu da aka kora sun hada da Sani Munzani mai shekaru 24;  Abubakar Auwalu, 26;  Abubakar Sani, 23 da  Muazu Hassan, 22. 

An samu labarin cewa sojojin sun kashe jami’in hukumar ta NDLEA ne a watan Maris din shekarar 2024 a lokacin da suka far wa jami’an NDLEA da suka tsayar da su a lokacin da suke bincike a mahadar Ramat da ke Bida.

FaÉ—an ya kai ga daba wa Chimetalo wuka a bayansa.

An kai jami’in zuwa FMC Bida inda daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa. 

Yayin da suke gudanar da bincike kan lamarin, jami’an ‘yan sandan da ke aiki da ‘A’ Division Bida sun gano bindigar jami’in a wani daji da ke kusa ba tare da gidan harsashi ba.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...