An kama mataimaki shugaban karamar hukuma saboda alaka da ‘yan bindiga

Sojoji dake aikin kakkabe yan ta’adda a jihar Zamfara da a kaiwa lakabi da Operation Sharar Daji sun kama mataimakin shugaban karamar hukumar Anka,Yahuza Ibrahim Wuya kan zarginsa da ake da alaka da masu garkuwa da mutane.

An kama shine ranar 13 ga watan Afirilu bisa dogaro da kwararan bayanan sirri da aka samu dake nuna alakarsa da barayi masu garkuwa da mutane a garuruwan Wuya da Sunke a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ta Operation Sharar Daji, Manjo Clement Abide ya fitar.

Ana zargin Yahuza Ibrahim yana taimakawa wajen sayar da shanu da jakunan da aka sace da kuma samarwa da barayin bayanai kan ayyukan jami’an tsaro da kuma yan banga.

“Ana kuma zarginsa da taimakawa wajen kubutar da wani kasurgumin mai sayar da bindigogi mai suna Sani Yaro daga gidan yarin Gusau,” a cewar sanarwar.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...