An kama manyan motoci maƙare da kayan abinci suna shirin fita daga Najeriya

A ranar Litinin ne Hukumar Sufuri ta Jihar Zamfara ta kama manyan motoci 50 da ke jigilar kayan abinci daga Najeriya zuwa Jamhuriyar Nijar.

Hukumar, wacce ke aiwatar da umarnin shugaban kasa da ke da nufin kawo karshen matsalar karancin abinci da tara kaya, ta hana motocin da ke cike da hatsi iri-iri fita.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne shugaban kasa Bola Tinubu ya umurci mutane mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu da sufeto janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun da kuma babban daraktan ma’aikatar harkokin gwamnati Yusuf Bichi da su hada kai da gwamnonin jahohi wajen dakile karancin kayan abinci.

An dauki matakin ne a yayin ganawar da shugaban kasar ya yi da gwamnoni a Abuja kan matsalar karancin abinci da aka samu a halin yanzu sakamakon hauhawar farashin man fetur bayan cire tallafin man fetur da kuma kasa girbi amfanin gonakin da manoma ke yi saboda ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...