An Kama Jirgin Ruwa Ɗauke Da Ɗanyen Man Fetur Na Sata A Bayelsa

Tantita Private Security Services Limited (TSSL) kamfanin samar da tsaro mai zaman kansa da gwamnatin tarayya ta bawa aikin yaƙi da satar ɗanyen man fetur a yankin Niger Delta ya kama wani jirgin ruwa ɗauke da man sata har lita dubu 80000 a jihar Bayelsa.

Warredi Enisuoh daraktan ayyukan yau da kullum na kamfanin ya ce an kama jirgin ne da tsakar daren ranar Lahadi a jihar Bayelsa aka kuma tasa keyarsa ya zuwa Oporozza dake jihar Delta.

Enusuoh ya ce jirgin mai suna MT Harbor Spirit an kama shi ne lokacin da yake ɗaukar mai daga rijiyar mai ta Segana dake gaɓar ruwan Bayelsa.

Ya ce an kama jirgin ruwan da haɗin gwiwar jami’an tsaron soja da na kamfanin na TSSL bayan da suka jima suna bibiyar ayyukan jirgin.

Enusuoh ya ƙara da cewa yan Najeriya 12 ne a cikin jirgin lokacin da aka tsare jirgin.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...