Wasu ‘Æ´an bindiga sun kai hari kan wani otal da ke birnin Nairobi a kasar Kenya.
An ji karar harbe-harben bindiga da fashewar wasu abubuwa a ginin da ke lardin Westlands, wanda otal din DusitD2 da wasu ofis-ofis ke ciki.
Kungiyar al-Shabab da ke da mazauni a Somalia ta dauki alhakin kai harin ko da yake ba ta yi karin bayani ba. Ganau sun hangi ‘yan bidiga hudu sun shiga ginin
Jama’a da ke cikin ginin sun yi ta fice wa daga cikinsa da rakiyar jami’an tsaro. An fitar da mutane da dama da suka yi jina-jina daga cikin ginin.