An jibge jami’an tsaro gabanin zaben gwamnan Ondo – AREWA News

Kasa da sa’o’i 24 suka rage kafin masu kada kuri’a su fita zuwa tashoshin zabe a jihar Ondo an jibge jami’an tsaro masu yawa dake gudanar da sintiri a Akure babban birnin jihar da kuma wasu garuruwa.

Mutane da dama sun ga jerin ayarin gamayyar jami’an tsaron da suka hada da sojoji, yan sanda, jami’an Civil Defence suna gudanar da sintiri na hadin gwiwa.

Ana dai fargabar samun rikici a zaben na ranar Asabar duba da yadda aka rika samun tashin hankali a lokacin da yan takarkarun ke gudanar da yakin neman zabe.

Ana ganin zaben na ranar Asabar karawa ne a tsakanin yan takara uku duk da cewa akwai sauran yan takara da suke wasu jam’iyu na daban.

Manyan yan takara a zaɓen sun hada da dan takarar jam’iyar APC kuma gwamna mai ci,Rotimi Akeredulu, sai Eyitayo Jegede na jam’iyar adawa ta PDP sai kuma Ajayi Agboola na jam’iyar ZLP wanda shi ne ke rike da mukamin mataimakin gwamnan jihar.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...