Kasa da sa’o’i 24 suka rage kafin masu kada kuri’a su fita zuwa tashoshin zabe a jihar Ondo an jibge jami’an tsaro masu yawa dake gudanar da sintiri a Akure babban birnin jihar da kuma wasu garuruwa.
Mutane da dama sun ga jerin ayarin gamayyar jami’an tsaron da suka hada da sojoji, yan sanda, jami’an Civil Defence suna gudanar da sintiri na hadin gwiwa.
Ana dai fargabar samun rikici a zaben na ranar Asabar duba da yadda aka rika samun tashin hankali a lokacin da yan takarkarun ke gudanar da yakin neman zabe.
Ana ganin zaben na ranar Asabar karawa ne a tsakanin yan takara uku duk da cewa akwai sauran yan takara da suke wasu jam’iyu na daban.
Manyan yan takara a zaɓen sun hada da dan takarar jam’iyar APC kuma gwamna mai ci,Rotimi Akeredulu, sai Eyitayo Jegede na jam’iyar adawa ta PDP sai kuma Ajayi Agboola na jam’iyar ZLP wanda shi ne ke rike da mukamin mataimakin gwamnan jihar.