Sabbin zababbun ‘yan majalisar dokokin Najeriya sun ki yarda tare da jan daga da kuma fitowa takarar mukamin kakakin majalisar wakilai, da za a kafa duk da cewa jam`iyyar APC mai mulki ta ce za ta kebe mukamin ga shiyya daya kawai.
Wasu jiga-jigan jam`iyyar dai na yin isharar da ke nuna cewa za a kebe mukamin Kakakin ne ga shiyyar kudu-maso-yammacin kasar, daga cikin shiyyoyi shida amma wasu `yan majalisar na cewa ba za ta sabu ba.
Ya zuwa yanzu dai wadanda suka fito takarar mukamin na shugaban majalisar wakilan Najeriyar sun zarta mutum goma, kuma kowanne ya ja daga da cewa shi ya fi cancanta.
Honorabul Muhammadu Umaru Bako daga shiyyar Arewa ta tsakiya, wanda yake cikin masu takarar ya ce, yankinsu ne ya fi dacewa da mukamin, idan aka yi la’akari da kason mukaman da wasu shiyyoyin suka samu.
Ya ce: ”Wannan naman guda shida a kan tebur, an dauka daya an ba Arewa maso yamma (mukamin shugaban kasa), an dauka mataimakin shugaban kasa an kai ma Kudu maso yamma, Senet an kai ma Arewa na gabas.
Ya ake so a yi da mu? Ba za a iya tauye mana hakki ba, gaskiyar magana ke nan.”
Dan majalisar ya kara da cewa, ”babu gudu ba ja da baya. Mu dai mun san cewa in za a yi mana adalci mu ne ya kamata, in ba a yi mana adalci kuma to shi ke nan adalci zai ba mu.”
Tun a kwanakin baya jam’iyyar APC mai mulkin kasar ta yi wata ganawa da ‘yan majalisar dokokin da za su kafa majalisar dokokin kasar ta tara.
A lokacin ta bayyana cewa za ta fito da tsarin rarraba mukaman majalisun a tsakanin shiyyoyin kasar cikin mako daya, amma har yanzu ba ta fito da tsarin ba.
Da BBC ta tambayi Sakataren walwala na jam’iyyar, Alhaji Ibrahim Masari, kan wannan magana sai ya ce, ba su kai ga zaman yanke wannan matsaya ba.
Sai dai yana ganin kila zuwa karshen makon da ake ciki majalisar zartarwa ta jam’iyyar ta APC, za ta zauna domin fitar da wannan matsaya.
Dangane da matakin da jam’iyyar ke neman dauka na rarraba mukaman har wasu ke kalubalantar hakan da cewa dole ne a bi tsarin dumokuradiyya, Alhaji Ibrahim ya ce hakan ba wata matsala ba ce da za ta iya kaiwa ga jam’iyyar ta yi asarar mukaman, kamar a baya ba.
Ya ce, dukkanin sabbin ‘yan majalisar sun yarda cewa jam’iyya ce take da wuka da nama, kuma duk mai yi mata biyayya wajibi ne ya amince da matsayin da za ta fito da shi.
Yayin da ake ta wannan ce-ce-ku-ce da rububi kan neman mukamin Kakakin majalisar wakilan ta Najeriya, har yanzu jam’iyyar ta APC ba ta iya shawo kan ‘ya’yanta ba da suke ja da matakinta na kebe mukamin shugaban majalisar dattawa ga shiyyar Arewa maso gabashin kasar ba, har ma kuma da ayyana wanda take son ya samu mukamin.
Wasu masu lura da al’amura dai na ganin idan jam’iyyar ba ta yi taka tsan-tsan ba, wadannan matsaloli za su iya jefa ta cikin rudani, har ma ta yi asarar mukaman.