An halaka mutane 6 a wani faɗa tsakanin ƴanbindiga da ƴanbanga

Mutane 6 ne suka rasa rayukansu a wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan bindiga da ’yan banga da aka fi sani da ‘Yan Sakai a karamar hukumar Gada a jihar Sakkwato.

‘Yan bangar, a cewar wata majiya a yankin da ta nemi a sakaya sunanta saboda yadda lamarin ya kasance, an ce sun dauki fansa ne kan kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa shugabansu, Alhaji Dahiru.

Shaidun gani-da-ido sun ce rikicin ya fara ne a lokacin da wani jagoran ‘yan banga kauyen Gidan Hashimu ya yi wani yunkuri na kama wasu barayin shanu.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar da ake zargin, a daidai lokacin da rikicin ya yi kamari, sun harbe shugaban ‘yan bangan har lahira, lamarin da ya janyo ramuwar gayya daga ‘yan banga.

Daya daga cikin shaidun gani da ido ya ce kafin isowar tawagar jami’an tsaron kasuwar, sama da mutum shida ne suka mutu.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...