Yan kwanaki bayan nasararsa a zabe, hukumar yan sanda ta gurfanar da Sanata Dino Melaye a gaban babbar kotun tarayya da ke Apo, Abuja a ranar Talata, 5 ga watan Maris kan tuhume-tuhume shida, ciki harda na yunkurin kashe kansa.
Daga wani rukuni na tuhumar, an zargi Sanata Melaye da yunkurin tserewa daga inda aka tsare shi.
Melaye wanda kwanan nan ya sake lashe kujerar satana mai wakiltan Kogi ta yamma na fuskantar zargin lalata kayayyakin yan sanda.
Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Sanata Melaye ya karyata aikata dukkanin laifuffukan da ake tuhumarsa a kai.
Rahoton ya kawo inda Justis Sylvanus Oriji yayi bayanin cewa yana sane da cewar kotu ta bayar da belin Melaye a lokacin da aka gurfanar dashi a gabansa a ranar 25 ga watan Yulin 2018, akan wannan tuhume-tuhumen.