An gurfanar da Melaye kwanaki kadan bayan ya lashe zabe

Yan kwanaki bayan nasararsa a zabe, hukumar yan sanda ta gurfanar da Sanata Dino Melaye a gaban babbar kotun tarayya da ke Apo, Abuja a ranar Talata, 5 ga watan Maris kan tuhume-tuhume shida, ciki harda na yunkurin kashe kansa.

Daga wani rukuni na tuhumar, an zargi Sanata Melaye da yunkurin tserewa daga inda aka tsare shi.

Melaye wanda kwanan nan ya sake lashe kujerar satana mai wakiltan Kogi ta yamma na fuskantar zargin lalata kayayyakin yan sanda.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Sanata Melaye ya karyata aikata dukkanin laifuffukan da ake tuhumarsa a kai.

Rahoton ya kawo inda Justis Sylvanus Oriji yayi bayanin cewa yana sane da cewar kotu ta bayar da belin Melaye a lokacin da aka gurfanar dashi a gabansa a ranar 25 ga watan Yulin 2018, akan wannan tuhume-tuhumen.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...