An bawa Elrufai sarauta a masarautar Ijebu

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru Elrufai ya samu sarautar gargajiya ta Gbobaniyi na kasar Ijebu dake jihar Ogun.

Oba Sikiru Kayode Adetona, shi ne ya bawa, Elrufai sarautar a wani biki da aka gudanar a ranar Asabar.

Elrufai shi ne mutum na farko daga yankin arewacin Najeriya da masauratar ta Ijebu ta bawa sarauta.

More from this stream

Recomended